Jam’iyyar Labour Party, LP, ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ba da fifiko wajen inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.
Sakataren jam’iyyar na kasa Umar Farouk Ibrahim ne ya yi wannan kiran a matsayin martani ga takun saka da aka samu a kasar nan.
An samu turmutsutsu a Oyo, Anambra, da kuma babban birnin tarayya, FCT, inda sama da mutane 50, ciki har da kananan yara suka mutu a lokacin rabon kayan abinci na karshen shekara.
A cikin wata sanarwa a ranar Litinin, sakataren LP, ya ce ‘yan Najeriya sun yanke shawarar yin kasada don ci gaba da rayuwa sakamakon tsadar rayuwa a kasar.
“Batun magana ita ce, akwai yunwa a cikin ƙasa. Talauci ne kawai ya sanya wasu ‘yan Najeriya ke diban mai a wuraren da hatsarin ya rutsa da su, lamarin da ya janyo tashin gobarar da ta janyo asarar rayuka.
“Wannan ya faru sau da yawa a cikin shekarar da ta gabata.
“Babban dalilin da ya sa mutane ke aikata laifuka shi ne yunwa. ‘Yan Najeriya miliyoyi sun fuskanci yunwa sakamakon wasu dalilai kamar hauhawar farashin kayayyaki da rashin tafiyar da tattalin arziki.
“Sake fasalin tattalin arzikin gwamnatin Tinubu ya jawo wa ‘yan Nijeriya wahalhalun da ba za a iya mantawa da su ba. Yunwa tana rikidewa zuwa annoba, kuma ba mutane da yawa ba ne za su iya tsira daga wannan yanayin,” in ji shi.
A cewarsa, ya kamata a yi amfani da albarkatun kasa wajen inganta jin dadin ‘yan kasar.
Ibrahim ya kara da cewa babu wani abu na zahiri da gwamnati ta yi domin magance matsalar yunwa da kuma duba irin talaucin da ake fama da shi a Najeriya, yana mai jaddada cewa dole ne gwamnati ta tashi tsaye ta hada ayyukanta.