fidelitybank

Tinubu a na fama da yunwa a Gwamnatin ka – LP

Date:

Jam’iyyar Labour Party, LP, ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ba da fifiko wajen inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

Sakataren jam’iyyar na kasa Umar Farouk Ibrahim ne ya yi wannan kiran a matsayin martani ga takun saka da aka samu a kasar nan.

An samu turmutsutsu a Oyo, Anambra, da kuma babban birnin tarayya, FCT, inda sama da mutane 50, ciki har da kananan yara suka mutu a lokacin rabon kayan abinci na karshen shekara.

A cikin wata sanarwa a ranar Litinin, sakataren LP, ya ce ‘yan Najeriya sun yanke shawarar yin kasada don ci gaba da rayuwa sakamakon tsadar rayuwa a kasar.

“Batun magana ita ce, akwai yunwa a cikin ƙasa. Talauci ne kawai ya sanya wasu ‘yan Najeriya ke diban mai a wuraren da hatsarin ya rutsa da su, lamarin da ya janyo tashin gobarar da ta janyo asarar rayuka.

“Wannan ya faru sau da yawa a cikin shekarar da ta gabata.

“Babban dalilin da ya sa mutane ke aikata laifuka shi ne yunwa. ‘Yan Najeriya miliyoyi sun fuskanci yunwa sakamakon wasu dalilai kamar hauhawar farashin kayayyaki da rashin tafiyar da tattalin arziki.

“Sake fasalin tattalin arzikin gwamnatin Tinubu ya jawo wa ‘yan Nijeriya wahalhalun da ba za a iya mantawa da su ba. Yunwa tana rikidewa zuwa annoba, kuma ba mutane da yawa ba ne za su iya tsira daga wannan yanayin,” in ji shi.

A cewarsa, ya kamata a yi amfani da albarkatun kasa wajen inganta jin dadin ‘yan kasar.

Ibrahim ya kara da cewa babu wani abu na zahiri da gwamnati ta yi domin magance matsalar yunwa da kuma duba irin talaucin da ake fama da shi a Najeriya, yana mai jaddada cewa dole ne gwamnati ta tashi tsaye ta hada ayyukanta.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp