fidelitybank

Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

Date:

Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta ba tare da ɓata lokaci ba kuma ba tare da wani sharaɗi ba” bayan kwana biyar na faɗa a kan iyakar ƙasashen biyu.

Faɗar ta yi sanadin mutuwar mutum aƙalla 33 tare da raba dubban mutane da muhallansu.

“Wannan babban mataki ne na farko wajen rage rikici da dawo da zaman lafiya da tsaro,” in ji firaministan Malaysia, Anwar Ibrahim, yayin da yake sanar da dakatar da faɗa yana mai cewa an cimma matsaya cewa za a daina faɗa daga ƙarfe 12 na dare.

A farko, Thailand ta ƙi amincewa da tayin shiga tsakani da Anwar ya bayar, sai dai ta amince daga bisani bayan shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba za a cigaba da tattaunawar haraji ba har sai “an daina faɗa”.

Tashin hankali a kan tsohuwar takaddamar kan iyaka ya ƙara ƙamari a watan Mayu bayan wani sojan Cambodia ya mutu a wata arangama.

Daga bisani kuma Thailand ta sanya takunkumi ga ‘yan ƙasa da yawon bude ido daga shiga Cambodia ta hanyar ƙasa, yayin da Cambodia ta haramta shigo da wasu kayayyaki daga Thailand.

Lamarin ya ƙara ta’azzara a makon da ya gabata, bayan wani soja dan Thailand ya rasa ƙafarsa a fashewar bam.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...

Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta...

Yansanda sun kama Sojoji cikin ‘ƴan ƙungiyar asiri’ a jihar Ogun

Rundunar 'yansanda reshen jihar Ogun, ta tabbatar da kama...

Yadda ambaliya ta shanye Adamawa

Rahotonni daga birnin Yola na jihar Adamawa na cewa,...

Yadda Jodan da Dubai ke jefa wa al’ummar Gaza abinci ta sama

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Jordan ta ce, jiragen...

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...
X whatsapp