fidelitybank

Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta

Date:

Ƙasashen Thailand da Cambodia sun amince da tsagaita wuta ba tare da ɓata lokaci ba kuma ba tare da wani sharaɗi ba” bayan kwana biyar na faɗa a kan iyakar ƙasashen biyu.

Faɗar ta yi sanadin mutuwar mutum aƙalla 33 tare da raba dubban mutane da muhallansu.

“Wannan babban mataki ne na farko wajen rage rikici da dawo da zaman lafiya da tsaro,” in ji firaministan Malaysia, Anwar Ibrahim, yayin da yake sanar da dakatar da faɗa yana mai cewa an cimma matsaya cewa za a daina faɗa daga ƙarfe 12 na dare.

A farko, Thailand ta ƙi amincewa da tayin shiga tsakani da Anwar ya bayar, sai dai ta amince daga bisani bayan shugaban Amurka Donald Trump ya ce ba za a cigaba da tattaunawar haraji ba har sai “an daina faɗa”.

Tashin hankali a kan tsohuwar takaddamar kan iyaka ya ƙara ƙamari a watan Mayu bayan wani sojan Cambodia ya mutu a wata arangama.

Daga bisani kuma Thailand ta sanya takunkumi ga ‘yan ƙasa da yawon bude ido daga shiga Cambodia ta hanyar ƙasa, yayin da Cambodia ta haramta shigo da wasu kayayyaki daga Thailand.

Lamarin ya ƙara ta’azzara a makon da ya gabata, bayan wani soja dan Thailand ya rasa ƙafarsa a fashewar bam.

hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp