fidelitybank

TCN zai yi gyare-gyaren ayyukansa na wutar lantarki a Abuja

Date:

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na (TCN), ya sanar da ayyukan gyare-gyare da za su shafi wutar lantarki a wasu sassan Birnin Tarayya (FCT).

TCN ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Babban Manajan Hulda da Jama’a, Ndidi Mbah, ya fitar a ranar Asabar.

Sanarwar ta ce injiniyoyin kamfanin za su gudanar da gyare-gyare a tashoshin rarraba wutar lantarki guda biyu daga ranar Asabar zuwa Lahadi.

Sanarwar ta kara da cewa daga karfe 9 na safe zuwa 1 na rana a ranar Asabar, za a gudanar da gyare-gyare akan injin samar da wuta mai karfin 60MVA da kayan aikin da ke da alaka da shi a tashar wutar lantarki ta Gwagwalada 330/132/33kV.

Haka kuma, daga karfe 9 na safe zuwa 10 na dare a ranar Lahadi, za a gudanar da gyare-gyare akan daya daga cikin injinan samar da wuta mai karfin 60MVA a tashar rarraba wutar lantarki ta Kukwaba 132/33kV.

A cewar TCN, wannan zai haifar da katsewar wutar lantarki a Wuye, EFCC, Asibitin Tarayya, Coca-Cola, Tashar Jirgin Kasa ta Idu, Citec, da Life Camp.

Sanarwar ta kara da cewa:

“Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) na sanar da jama’a cewa injiniyoyinsa za su gudanar da ayyukan gyare-gyare a tashoshin wutar lantarki guda biyu.

“A yau, Asabar, 28 ga Disamba, 2024, daga karfe 9 na safe zuwa 1 na rana, za a gudanar da gyare-gyare akan injin samar da wuta mai karfin 60MVA da kayan aikin da ke da alaka da shi a tashar wutar lantarki ta Gwagwalada 330/132/33kV.

“A wannan lokacin, kamfanin Abuja DisCo ba zai iya samar da wutar lantarki ga abokan ciniki a Gwagwalada da kewaye ba har tsawon sa’o’i hudu

“TCN ta ba da hakuri kan wannan rashin jin dadi da za ta iya haifarwa, musamman a wannan lokacin karshen shekara da bukukuwan Kirsimeti. Duk da haka, yana da muhimmanci a gudanar da gyare-gyare kamar yadda aka tsara don inganta aikin kayan aikin wuta.”

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp