fidelitybank

TCN zai yi gyare-gyaren ayyukansa na wutar lantarki a Abuja

Date:

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na (TCN), ya sanar da ayyukan gyare-gyare da za su shafi wutar lantarki a wasu sassan Birnin Tarayya (FCT).

TCN ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Babban Manajan Hulda da Jama’a, Ndidi Mbah, ya fitar a ranar Asabar.

Sanarwar ta ce injiniyoyin kamfanin za su gudanar da gyare-gyare a tashoshin rarraba wutar lantarki guda biyu daga ranar Asabar zuwa Lahadi.

Sanarwar ta kara da cewa daga karfe 9 na safe zuwa 1 na rana a ranar Asabar, za a gudanar da gyare-gyare akan injin samar da wuta mai karfin 60MVA da kayan aikin da ke da alaka da shi a tashar wutar lantarki ta Gwagwalada 330/132/33kV.

Haka kuma, daga karfe 9 na safe zuwa 10 na dare a ranar Lahadi, za a gudanar da gyare-gyare akan daya daga cikin injinan samar da wuta mai karfin 60MVA a tashar rarraba wutar lantarki ta Kukwaba 132/33kV.

A cewar TCN, wannan zai haifar da katsewar wutar lantarki a Wuye, EFCC, Asibitin Tarayya, Coca-Cola, Tashar Jirgin Kasa ta Idu, Citec, da Life Camp.

Sanarwar ta kara da cewa:

“Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) na sanar da jama’a cewa injiniyoyinsa za su gudanar da ayyukan gyare-gyare a tashoshin wutar lantarki guda biyu.

“A yau, Asabar, 28 ga Disamba, 2024, daga karfe 9 na safe zuwa 1 na rana, za a gudanar da gyare-gyare akan injin samar da wuta mai karfin 60MVA da kayan aikin da ke da alaka da shi a tashar wutar lantarki ta Gwagwalada 330/132/33kV.

“A wannan lokacin, kamfanin Abuja DisCo ba zai iya samar da wutar lantarki ga abokan ciniki a Gwagwalada da kewaye ba har tsawon sa’o’i hudu

“TCN ta ba da hakuri kan wannan rashin jin dadi da za ta iya haifarwa, musamman a wannan lokacin karshen shekara da bukukuwan Kirsimeti. Duk da haka, yana da muhimmanci a gudanar da gyare-gyare kamar yadda aka tsara don inganta aikin kayan aikin wuta.”

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp