Kamfanin rarraba wutar lantarki ƙasa TCN, ya ce, ma’aikatansa sun fara gyarawa tare da sake turken wutar lantarki mai lamba 16 da ya lalace a kauyen Gunduwawa da ke karamar hukumar Gezawa a Jihar Kano.
Wata tirela da ke dauke da kwantena ta afkawa turken, inda ta lalata ta tare da kawo cikas a wasu yankunan.
Sai dai Babban Manaja na Hulda da Jama’a, Ndidi Mbah a cikin wata sanarwa da ya fitar ya ce, dan kwangilar ya koma bakin aiki a wurin duk da cewa ya ba da tabbacin cewa, za a kammala aikin gysrsn nan da ranar 22 ga Agusta, 2024.