Tawagar Super Eagles ta je birnin Abidjan na kasar Cote d’Ivoire, domin buga gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 2023.
‘Yan wasan da jami’ansu wadanda suka yi sanye da kayan gargajiya na Afirka, sun bar filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas zuwa Abidjan da safiyar Laraba.
Tawagar ta isa Legas daga Abu Dhabi na Hadaddiyar Daular Larabawa a ranar Talata.
Kungiyar Jose Peseiro ta shafe mako guda a Abu Dhabi don kammala dabarun AFCON.
Gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu ne ya shirya musu liyafar cin abincin dare a daren ranar Talata.
Zakarun Afirka sau uku za su kasance a otal din Pullman da ke Abidjan.
Wasan farko na Najeriya shine da Nzalang Nacional ta Equatorial Guinea a filin wasa na Alassanne Quattara, Ebimpe, ranar Lahadi.