Kungiyar masu fafutukar kare hakkin doka, wadda ta kunshi lauyoyi, ta bayyana cewa tana shirin shigar da kara a gaban babbar kotun tarayya, domin kalubalantar sabuwar dokar taken Najeriya.
Kungiyar wacce ta sanar da matakin a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren kungiyar, Dr Tonye Clinton Jaja, ya fitar a yau Juma’a, ta ce kafa dokar da ta haifar da sabon taken Najeriyar ba a bi ka’idojin tsarin mulki ba.
A cewar sanarwar, ba a gudanar da jin ra’ayin jama’a ba kafin a samar da dokar kamar yadda ake bukata a karkashin sashe na 60 na kundin tsarin mulkin kasa na 1999.
Tinubu dai ya rattaba hannu kan dokar wakar ta kasa, wadda ta zama doka, inda ya sake dawo da tsohuwar wakar ta kasa, mai suna ‘Nigeria we heil you’ a matsayin taken Najeriya.