Biyo bayan rashin gamsuwa da sakamakon zaben shugaban kasa da aka kammala, tawagar lauyoyin jam’iyyar Labour ta isa ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a Abuja domin duba kayan aiki.
Tashar talabijin ta Channels ta rawaito cewa a halin yanzu tawagar na ganawa da jami’an hukumar.
Ganawar da jami’an hukumar ta INEC, wanda ke gudana a hedkwatar hukumar ta kasa, na da nufin fara aikin duba kayan zaben da aka yi amfani da su a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu.
Karanta Wannan: Obi ya mayar da martani ga Wike
Tawagar wacce ke da lauyoyi kusan 60 karkashin jagorancin Dr Livy Uzoukwu. Ana sa ran za su yi wa ‘yan jarida bayani bayan taron