fidelitybank

Tawagar gwamnatin Kano sun tafi Edo kan kisan matafiya a Uromi

Date:

Wakilan gwamnatin jihar Kano ƙarƙashi jagorancin mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam Gwarzo sun tafi jihar Edo domin faɗaɗe bincike tare da tattauna batun kisan matafiya ƴan arewa da aka yi a garin Uromi da ke jihar wadda ke kudancin Najeriya.

Tawagar ta ƙunshi shi mataimakin gwamnan, da Sarkin Rano Ambasada Mohammad Isa Umar da kwamishinonin addini da na ƙananan hukumomi da na ayyuka na musamman da ta harkokin mata da shugaban ƙaramar hukumar Bunkure da sauransu, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin gwamnan jihar, Ibrahim Garba Shuaibu ya nuna a wata sanarwa da ya fitar.

Da yake jawabi a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano kafin tafiyarsu, Gwarzo ya ce za su tafi Edo ne domin su yi bincike, “ta hanyar tattaunawa domin gano haƙiƙanin yadda lamarin ya auku domin samar da matsaya mai inganci.”

Ya ce ba wai za su je bincike ba ne kawai, “zuwan zai taimaka wajen ƙara sulhunta tsakanin al’ummomi domin kare sake aukuwar lamarin.”

A baya dai gwamnan jihar Edo Monday Okpebholo ya ziyarci Kano domin jajanta wa iyalan waɗanda aka kashe a jiharsa, inda a lokacin ziyarar gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya buƙaci a biya diyyar waɗanda aka kashe ɗin, sannan a yi holen waɗanda aka kama da zargin kisan.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp