fidelitybank

Tawagar gwamnatin Kano sun tafi Edo kan kisan matafiya a Uromi

Date:

Wakilan gwamnatin jihar Kano ƙarƙashi jagorancin mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam Gwarzo sun tafi jihar Edo domin faɗaɗe bincike tare da tattauna batun kisan matafiya ƴan arewa da aka yi a garin Uromi da ke jihar wadda ke kudancin Najeriya.

Tawagar ta ƙunshi shi mataimakin gwamnan, da Sarkin Rano Ambasada Mohammad Isa Umar da kwamishinonin addini da na ƙananan hukumomi da na ayyuka na musamman da ta harkokin mata da shugaban ƙaramar hukumar Bunkure da sauransu, kamar yadda wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin gwamnan jihar, Ibrahim Garba Shuaibu ya nuna a wata sanarwa da ya fitar.

Da yake jawabi a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano kafin tafiyarsu, Gwarzo ya ce za su tafi Edo ne domin su yi bincike, “ta hanyar tattaunawa domin gano haƙiƙanin yadda lamarin ya auku domin samar da matsaya mai inganci.”

Ya ce ba wai za su je bincike ba ne kawai, “zuwan zai taimaka wajen ƙara sulhunta tsakanin al’ummomi domin kare sake aukuwar lamarin.”

A baya dai gwamnan jihar Edo Monday Okpebholo ya ziyarci Kano domin jajanta wa iyalan waɗanda aka kashe a jiharsa, inda a lokacin ziyarar gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya buƙaci a biya diyyar waɗanda aka kashe ɗin, sannan a yi holen waɗanda aka kama da zargin kisan.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp