Masu sa ido na hukumar kwallon kafar Afirka CAF, sun duba wuraren da Najeriya ta sanya a gaba na karɓar bakwa cin gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 2025.
Najeriya ta gabatar da wani shiri na hadin gwiwa da makwabciyarta Jamhuriyar Benin, domin karbar bakuncin gasar duk shekara.
Tawagar ta CAF ta leka filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja, da Godswill Akpabio International Stadium, Uyo, Stephen Keshi Stadium, Asaba da Teslim Balogun, Legas.
Hukumar ta kuma duba filin wasa na Samuel Ogbemudia da ke birnin Benin da kuma filin wasa na Ahmadu Bello da ke Kaduna.
Tawagar ta samu rakiyar jami’an hukumar kwallon kafa ta Najeriya NFF.
Masu binciken za su kuma duba filin wasa na Charles de Gaulle, Porto Novo a Jamhuriyar Benin.
Idan dai ba a manta ba Najeriya ce ta dauki nauyin gasar ta AFCON a shekarar 2000 da Ghana.