fidelitybank

Tattalin arzikin Najeriya zai haɓaka a 2025 zuwa 2026 – Bankin Duniya

Date:

Bankin Duniya ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Najeriya zai haɓaka da aƙalla kashi 3.6 a tsakanin shekarar 2025 zuwa 2026.

Bankin ya bayyana haka ne a rahotonsa na hasashen tattalin arzikin duniya na 2025 da ya fitar a ranar Alhamis, 17 ga watan Janairu mai taken Global Economic Prospects January 2025.

“Tattalin arzikin yankin hamadar Afirka zai haɓaka da kashi 4.1 a shekarar 2025, da kuma kashi 4.3 a shekarar 2026,”

Rahoton ya ƙara da cewa, “a Najeriya kuma, ana hasashen tattalin arzikin ƙasar zai haɓaka da aƙalla kashi 3.6 a tsakanin shekarar 2025-26. Ana kuma hasashen hauhawar farashin kayayyaki zai ragu,” kamar yadda tashar Channels ta ruwaito daga rahoton.

Haka kuma rahoton ya ƙara da cewa man fetur da ƙasar ke samarwa zai ƙaru a tsakankanin lokacin da ake hasashen haɓakar tattalin arzikin ƙasar, amma duk da haka ba zai kai asalin abin da OPEC ta yi hasashen ƙasar za ta riƙa samarwa ba. In ji BBC.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp