fidelitybank

Tattalin arzikin Najeriya ya karu – NBS

Date:

Hukumar ƙididdiga ta ƙasa, wato NBS, ta ce tattalin arzikin Najeriya ya bunƙasa da kashi 3.46 a rubu’i na uku na wannan shekarar ta 2024.

Wannan nasarar ta samu ne a cikin sauri idan aka kwatanta da rubu’in biyu na farko da shekarar ta 2024, kamar yadda rahoton NBS ya nuna.

Sai dai duk da bunƙasar ta tattazlin arzikin, wato kashi 3.19 a rubu’i na biyu, da 2.98 a rubu’i na farko, har yanzu ba a kai ga samun nasarar bunƙasa tattalin arzikin ƙasar da kashi 6 ba kamar yadda gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ta yi alƙawari.

Nasarar da aka samu ba ta rasa nasaba da ci gaban da aka samu a ɓangaren harkokin tattalin arziki da suka shafi bankuna da intanet, wanda ya inganta tattalin arzikin ƙasar da kashi 50 a tsakanin Yuli da Satumba.

Wasu matakan da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya ɗauka a makonsa na farko a mulki sun sa an yi tunanin zai bunƙasa tare da inganta tattalin arzikin ƙasar, wada ita ce mafi girman tattalin arzikin nahiyar.

Amma bayan wata 18 da fara mulkin, manyan matakan da ya ɗauka – cire tallafin man fetur da karya darajar naira – sun jawo tsadar rayuwa da aka daɗe ba a gani ba a ƙasar a cikin shekaru masu yawa, amma har yanzu ba a fara gani a ƙasa ba.

Ɓangaren man fetur na ƙasar, wanda shi ne kan gaba wajen samar da kuɗin shiga ga gwamnatin ƙasar, ya samu bunƙasa da kashi 5.17, inda gangar man da ake fitarwa a ƙasar ya ƙaru zuwa ganga miliyan 1.47 a rana, maimakon ganga miliyan 1.41 da ake fitarwa a rubu’i na biyu na shekarar.

An samu koma-baya ne a ɓangaren noma daga kashi 1.41 a rubu’i na biyu, zuwa 1.14 a rubu’i na ukun, sannan ɓangaren masana’antu ya samu tagomashi daga 2.18 zuwa 3.35 a watan Afrilu zuwa Yuni.

Bankin bayar da lamuni ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Najeriya zai haɓaka da kashi 2.9 a shekarar 2024, da kuma 3.2 a shekara mai zuwa.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp