fidelitybank

Tattalin arzikin Najeriya ya haɓaka sosai – Bankin Duniya

Date:

Bankin Duniya ya ce, tattalin arzikin Najeriya haɓɓaka fiye da kowanne lokaci cikin shekara goma da ta gabata, sakamakon wasu muhimman gyare-gyaren da gwamnati ta aiwatar sai dai kuma Bankin Duniyan ya gargadi cewa hauhawar farashin kayayyaki na ci gaba da addabar miliyoyin ƴan ƙasar.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Bankin Duniya ya fitar wa manema labarai, inda ya bayyana cewa ƙarfin tattalin arziƙin Najeriya na cikin gida ya ƙaru da kashi 4.6 cikin 100 a zangon ƙarshe na shekara ta 2024.

Wannan, in ji Bankin Duniya ya kai jimillar ci gaban tattalin arziki na shekara zuwa kashi 3.4 cikin 100 – mafi girma tun shekarar 2014, baya ga farfaɗowar da aka samu daga lokacin annobar korona.

Rahoton ya danganta wannan cigaba ne ga ci gaban da ake samu a ɓangaren man fetur da iskar gas, da kuma ƙaruwar zuba jari da bunƙasar fasahar zamani da harkar kudi.

“Duk da wannan ci gaba, ɓangaren noma ya ci gaba da tafiyar hawainiya, inda ya karu da kashi 1.2 cikin 100 kacal a shekarar 2024,” in ji Bankin.

Bankin ya kara da cewa, “Wannan ƙarancin ci gaba ya samo asali ne daga rashin tsaro a yankin tsakiyar ƙasar da aka fi yin noma, da kuma hauhawar farashin kayayyakin noma kamar taki da man fetur.”

“Wadannan kalubalen suna da tasiri kai tsaye ga samar da abinci da kuma hauhawar farashin kayan masarufi, wanda ke ƙara matsin rayuwa ga miliyoyin ‘yan Najeriya,” in ji rahoton.

Bankin Duniya ya yaba wa gwamnatin shugaban Bola Ahmed Tinubu saboda ɗaukar matakan gyaran tattalin arziki tun bayan hawansa mulki a watan Mayun 2023.

Daga cikin wadannan gyare-gyare har da cire tallafin man fetur da ƙoƙarin farfaɗo da darajar Naira. Sai dai kuma rahoton ya ce waɗannan matakan sun haifar da matsin rayuwa ga al’umma da dama, musamman talakawa

sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp