fidelitybank

Tattalin arzikin Najeriya ya haɓaka sosai – Bankin Duniya

Date:

Bankin Duniya ya ce, tattalin arzikin Najeriya haɓɓaka fiye da kowanne lokaci cikin shekara goma da ta gabata, sakamakon wasu muhimman gyare-gyaren da gwamnati ta aiwatar sai dai kuma Bankin Duniyan ya gargadi cewa hauhawar farashin kayayyaki na ci gaba da addabar miliyoyin ƴan ƙasar.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Bankin Duniya ya fitar wa manema labarai, inda ya bayyana cewa ƙarfin tattalin arziƙin Najeriya na cikin gida ya ƙaru da kashi 4.6 cikin 100 a zangon ƙarshe na shekara ta 2024.

Wannan, in ji Bankin Duniya ya kai jimillar ci gaban tattalin arziki na shekara zuwa kashi 3.4 cikin 100 – mafi girma tun shekarar 2014, baya ga farfaɗowar da aka samu daga lokacin annobar korona.

Rahoton ya danganta wannan cigaba ne ga ci gaban da ake samu a ɓangaren man fetur da iskar gas, da kuma ƙaruwar zuba jari da bunƙasar fasahar zamani da harkar kudi.

“Duk da wannan ci gaba, ɓangaren noma ya ci gaba da tafiyar hawainiya, inda ya karu da kashi 1.2 cikin 100 kacal a shekarar 2024,” in ji Bankin.

Bankin ya kara da cewa, “Wannan ƙarancin ci gaba ya samo asali ne daga rashin tsaro a yankin tsakiyar ƙasar da aka fi yin noma, da kuma hauhawar farashin kayayyakin noma kamar taki da man fetur.”

“Wadannan kalubalen suna da tasiri kai tsaye ga samar da abinci da kuma hauhawar farashin kayan masarufi, wanda ke ƙara matsin rayuwa ga miliyoyin ‘yan Najeriya,” in ji rahoton.

Bankin Duniya ya yaba wa gwamnatin shugaban Bola Ahmed Tinubu saboda ɗaukar matakan gyaran tattalin arziki tun bayan hawansa mulki a watan Mayun 2023.

Daga cikin wadannan gyare-gyare har da cire tallafin man fetur da ƙoƙarin farfaɗo da darajar Naira. Sai dai kuma rahoton ya ce waɗannan matakan sun haifar da matsin rayuwa ga al’umma da dama, musamman talakawa

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...
X whatsapp