fidelitybank

Tattalin arziƙin Najeriya ya haɓɓaka

Date:

Tattalin arziƙin Najeriya ya haɓɓaka a rubu’i na huɗu na shekarar 2024, haɓɓaka mafi sauri a cikin shekara uku, kamar yadda alƙaluma suka nuna a yau Talata.

Arziƙin cikin gida na Najeriya ya haɓɓaka da kashi 3.84%, sama da kashi 3.46% da aka samu a rubu’i na uku na shekarar ta 2024.

A rubu’i na biyu na shekarar ta 2024 tattalin arziƙin ya haɓɓaka ne da kashi 3.19% yayin da rubu’i na farko kuma ya haɓɓaka da kashi 2.98%.

Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta ce ɓangaren tafiyar da ayyuka na tattalin arziƙin shi ne kan gaba wajen haɓɓaka, da kashi 5.7% idan aka kwatanta da shekarar da ta gabace ta.

A shekarar ta 2024 jimilla, tattalin arziƙin Najeriya ya haɓɓaka ne da kashi 3.40% idan aka kwatanta da kashi 2.74% a 2023.

Duk da haka, haɓɓakar ba ta cimma alƙawarin da shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya ɗauka na haɓɓaka tattalin arziƙin ƙasar da kashi 6% ba a shekarar ta 2024.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp