fidelitybank

Tattalin arziƙin Najeriya ya haɓɓaka

Date:

Tattalin arziƙin Najeriya ya haɓɓaka a rubu’i na huɗu na shekarar 2024, haɓɓaka mafi sauri a cikin shekara uku, kamar yadda alƙaluma suka nuna a yau Talata.

Arziƙin cikin gida na Najeriya ya haɓɓaka da kashi 3.84%, sama da kashi 3.46% da aka samu a rubu’i na uku na shekarar ta 2024.

A rubu’i na biyu na shekarar ta 2024 tattalin arziƙin ya haɓɓaka ne da kashi 3.19% yayin da rubu’i na farko kuma ya haɓɓaka da kashi 2.98%.

Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta ce ɓangaren tafiyar da ayyuka na tattalin arziƙin shi ne kan gaba wajen haɓɓaka, da kashi 5.7% idan aka kwatanta da shekarar da ta gabace ta.

A shekarar ta 2024 jimilla, tattalin arziƙin Najeriya ya haɓɓaka ne da kashi 3.40% idan aka kwatanta da kashi 2.74% a 2023.

Duk da haka, haɓɓakar ba ta cimma alƙawarin da shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya ɗauka na haɓɓaka tattalin arziƙin ƙasar da kashi 6% ba a shekarar ta 2024.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp