fidelitybank

Tasirin Najeriya na zubewa a Afrika – Obasanjo

Date:

Masana harkokin dfplomasiyya a Najeriya, sun fara tofa albarkacin bakinsu a kan wani furuci da tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya yi cewa, tasirin Najeriya a duniya yana raguwa, musamman ma a kan kasashen nahiyar Afirka.

Wasu masana na ganin cewa akwai gaskiya a cikin maganar, suna danganta lamarin da rashin ƙwararrun masu ba da shawara ga shugabanni da kuma rashin aiki da ita idan an ba su.

Tsohon shugaban, Cif Olusegun Obasanjo, ya yi wannan furucin ne a wajen wani bikin ƙaddamar da littafi a kansa, musamman ma yadda ya shahara wajen rubuta wa shugabannin Najeriya wasikar bankada ko tonun silili.

Ya ce tasirin kasar na fada a ji da kuma dadadden kallon da ake mata na babbar Yaya, kuma rumfa sha shirgi na ci gaba da raguwa musamman ma a kan kasashen nahiyar Afirka, sakamakon gazawa ko rashin tabuka abin kirki wajen jagorantar kannen nata.

Cif Obasanjon ya buga misali da wata gazawa da ya ce Najeriya ta yi wajen daidaita tsakanin shugabanni da Ć´an tawaye a kasar Chadi – lamarin da sai da Ć™asar Qatar ta dako gari daga nahiyar Asiya ta je ta shiga tsakani.

Tuni dai wasu masana huldar jakadanci suka fara tofa nasu albarkacin bakin a kan wannan maganar.

Ambasada Sulaiman Dahiru, tsohon jakadan Najeriya ne, wanda ya ce duk da cewa Cif Obasanjo kan ji babu wanda ya yi komai in ba shi ba…a wannan ɓigiren ya fadi gaskiya.

Sai dai na tambayi Ambasada Sulaiman Dahiru ko da wani abu da Najeriyar za ta yi don mai da martabar tata ta jagora ga kasashen nahiyar Afirkan?

A shekarun baya, an yi zamanin da Najeriya ta yi tasiri a kan kasashen Afirka da wasu kasashen duniya, musamman irin rawar da ta taka wajen yaki da nuna launin fata a kasar Afirka ta kudu da wasu makwabtanta.

Akwai ma lokacin da kasa irin Amurka ba ta daukar wani mataki a kan Afirka sai ta nemi shawarar Najeriya.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaÉ—i masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga FalasÉ—inawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen É—an gwagwarmayar nan kuma É—an jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp