Masana harkokin dfplomasiyya a Najeriya, sun fara tofa albarkacin bakinsu a kan wani furuci da tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya yi cewa, tasirin Najeriya a duniya yana raguwa, musamman ma a kan kasashen nahiyar Afirka.
Wasu masana na ganin cewa akwai gaskiya a cikin maganar, suna danganta lamarin da rashin ƙwararrun masu ba da shawara ga shugabanni da kuma rashin aiki da ita idan an ba su.
Tsohon shugaban, Cif Olusegun Obasanjo, ya yi wannan furucin ne a wajen wani bikin ƙaddamar da littafi a kansa, musamman ma yadda ya shahara wajen rubuta wa shugabannin Najeriya wasikar bankada ko tonun silili.
Ya ce tasirin kasar na fada a ji da kuma dadadden kallon da ake mata na babbar Yaya, kuma rumfa sha shirgi na ci gaba da raguwa musamman ma a kan kasashen nahiyar Afirka, sakamakon gazawa ko rashin tabuka abin kirki wajen jagorantar kannen nata.
Cif Obasanjon ya buga misali da wata gazawa da ya ce Najeriya ta yi wajen daidaita tsakanin shugabanni da ƴan tawaye a kasar Chadi – lamarin da sai da ƙasar Qatar ta dako gari daga nahiyar Asiya ta je ta shiga tsakani.
Tuni dai wasu masana huldar jakadanci suka fara tofa nasu albarkacin bakin a kan wannan maganar.
Ambasada Sulaiman Dahiru, tsohon jakadan Najeriya ne, wanda ya ce duk da cewa Cif Obasanjo kan ji babu wanda ya yi komai in ba shi ba…a wannan ɓigiren ya fadi gaskiya.
Sai dai na tambayi Ambasada Sulaiman Dahiru ko da wani abu da Najeriyar za ta yi don mai da martabar tata ta jagora ga kasashen nahiyar Afirkan?
A shekarun baya, an yi zamanin da Najeriya ta yi tasiri a kan kasashen Afirka da wasu kasashen duniya, musamman irin rawar da ta taka wajen yaki da nuna launin fata a kasar Afirka ta kudu da wasu makwabtanta.
Akwai ma lokacin da kasa irin Amurka ba ta daukar wani mataki a kan Afirka sai ta nemi shawarar Najeriya.