fidelitybank

Tashin Hankali: Mutum 12 sun kone kurmus a Kano

Date:

Akalla mutane 12 ne suka kone kurmus a wani hatsarin mota da ya afku a garin Tsamawa da ke karamar hukumar Garun Malam a jihar Kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar, SFS Saminu Abdullahi ya raba wa manema labarai a ranar Talata.

Ya ce, “Mun samu kira daga wani Isah Mai-Fetur da misalin karfe 3:00 na rana cewa, wata motar bas ta Hiace da wata motar bas J5 sun yi karo wuta nan take ta kama. ,Bayan samun labarin, mun aika da tawagar mu cikin gaggawa zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 3:12 na rana domin ceto wadanda abin ya shafa,” in ji sanarwar.

Ya kuma ce, mutane 11 da ke cikin motar Hiace sun taho ne daga hanyar Zariya zuwa Kano, yayin da mutum daya a cikin motar J5-bus shi ma ya na zuwa Kano daga Zariya.

Abdullahi ya ce, dukkan mutanen 12 sun kone kurmus, kamar yadda ya ce, hatsarin ya faru ne da gudun wuce sa’a da su ka yi.

Ya kuma shawarci masu ababen hawa da su rinka tuka mota a hankali domin gujewa abubuwan da ba a zata ba.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp