fidelitybank

Tashin Hankali: Mutane 7 sun ci abinci mai guba sun mutu a Zamfara

Date:

Akalla mutane bakwai ne aka tabbatar da mutuwarsu, sakamakon gubar abinci a kauyen Danbaza da ke karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara.

Lamarin ya faru ne bayan ‘yan uwa sun ci Dambu, wanda aka shirya a matsayin abincin dare.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa, wadanda suka mutu, matan aure biyu da ‘ya’yansu biyar, sun mutu nan da nan bayan an gama cin abinci.

A cewar wani dan uwa, Alhaji Muhammad Kabir, da mutane suka gama cin abincin, hudu daga cikin wadanda suka mutu nan take, yayin da uku kuma aka garzaya da su asibiti inda likitoci suka tabbatar da cewa sun mutu.

“An zargi wadanda suka mutu da amfani da guba wajen dafa abincin,” in ji shi.

Tuni dai aka yi jana’izar mutanen bakwai da suka mutu a garinsu na Danbaza, kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Shugaban karamar hukumar Maradun, Umar Mu’azu, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an aika wakilai daga karamar hukumar domin jajantawa iyalan mamatan.

Majalisar karamar hukumar ta bukaci ‘yan uwa da su karbi wannan rashi a matsayin iznin Allah tare da addu’ar Allah ya baiwa iyalan hakurin jure rashin.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp