Kamfanin man fetur na kasa (NNPC), ya sha alwashin kara yawan man da ake hakowa biyo bayan tashin farashin gangar danyen mai zuwa dala 105 a ranar Talata.
Manajan daraktan kamfanin na NNPC, Mele Kyari, ya yi wannan alwashi a lokacin da yake jawabi a taron makamashi na kasa da kasa na Najeriya na 2022 da ke gudana a Abuja ranar Talata.
Kyari ya ce, karuwar yawan man da ake hakowa a kasar ya zama dole, domin samun riba daga tashin farashin danyen mai.
Ya ce, “Dole ne mu share albarkatun da muke ciki a yau tare da dorewar canjin yanayi ta hanyar juriya har zuwa shekarar 2060.