An shiga rana ta uku a tarzomar da ake yi a birnin Los Angeles na jihar California ta Amurka inda masu zanga-zanga ke Ɗauki-ba-daɗi da dakarun tsaron Ƙasa da Shugaba Trump ya tura domin kwantar da zanga-zangar da ta Ɓarke sakamakon kamen baƙin haure.
Dakarun tsaron da Shugaban ya tura saɓanin ra’ayin gwamnan jihar da kuma shugabar birnin suna amfani da hayaƙi mai sa hawaye da harsashin roba wajen tarwatsa masu tarzomar.
Yayin da zanga-zangar da ta rikiɗe ta zama tarzoma ta shiga kwana na uku, lamarin na ci gaba da ƙazanta inda masu tarzomar suke ƙona motoci da tayoyi kuma dakarun tsaron da ‘yansanda da ke artabu da su, sun kama gommansu.
Shugaba Trump ya bayyana masu tarzomar da gungun masu tayar da hankali da tawaye, yana mai cewa dole ne a tabbatar da doka da oda.