Shugaban kasar Guinea Bissau, Umaro Sissoco Embaló, ya tabbatar da cewa, lamura sun daidaita bayan yunkurin juyin mulkin da bai yi nasara ga Dimukradiyya ba.
A lokacin da ya yi wa ‘yan kasar jawabi, shugaban Sissoco Embalo, ya kuma ce, an kashe yawancin jami’an tsaro a harin.
Sai dai ya ce, “Sam ban karaya ba, a lokacin da aka zabe ni shugaban kasa na yi alkawarin abubuwa biyu, yaki da rashawa da safarar muggan makamai”. A cewar Umaro.