Ministan Kimiyya, Fasaha, da Ƙirƙiri, Dr Ogbonnaya Onu, ya ce, taron tattalin arzikin duniya ya nuna ci gaban da Najeriya ta samu a fagen fafatawa a duniya daga matsayi na 124 a 2015 da 2016 zuwa 114 a 2018 da 2019.
Onu, wanda ya bayyana hakan a wajen taro karo na 20 na majalisar kula da kimiyya, fasaha da kirkire-kirkire ta kasa (NCSTI) a Abuja ranar Alhamis, ya ce kasashe 140 ne suka shiga wannan matsayi.
Ya ce, tsare-tsare irin su dabarun yin gasa a cikin albarkatun kasa da bunkasar kayayyaki, tare da dokar shugaban kasa ta 5 sun taimaka wajen wannan ci gaba.
Ya kuma kara da cewa, a shekarar 2019, takardun mallaka da hukumar kula da fasahar kere-kere ta kasa (NOTAP), karkashin kulawar ma’aikatarsa ta bayar, sun ba da gudummawar kashi 65 cikin 100 na dukiyoyin da aka samu a kasar nan.
Onu ya shawarci jihohin su tabbatar sun yi amfani da kudurorin da majalisar ta fitar wajen tsara hanyoyin ci gaban jihohinsu daban-daban.