fidelitybank

Taron kolin ECOWAS: Osibanjo ya nufi kasar Ghana

Date:

A yau ne mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo zai tafi birnin Accra na kasar Ghana domin wakilcin Najeriya a wani babban taron koli na kungiyar ECOWAS kan harkokin siyasa a kasar Mali da sauran sassan yankin.

Wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Laolu Akande ya fitar, ta ce, a wajen taron, Osinbajo zai bi sahun sauran shugabannin kasashen Yammacin Afirka, domin duba irin ci gaban da gwamnatin mulkin sojan Mali ta samu kan komawar kasar bisa tafarkin dimokuradiyya.

Taron zai karba tare da yin la’akari da sabon rahoto daga mai shiga tsakani na ECOWAS a Mali, tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, wanda ya ziyarci Bamako tsakanin 18 zuwa 20 ga watan Maris domin ganawa da shugaban mulkin soja. Shugabannin kasashen za su kuma duba halin da ake ciki a Jamhuriyar Burkina Faso da Guinea.

Bayan da sojoji suka kwace iko da gwamnatoci a Mali, Guinea da Burkina Faso, tare da kakaba takunkumi kan gwamnatin mulkin soja a wadannan kasashe, shugabannin ECOWAS a taron da suka yi na karshe a watan Fabrairu sun tabbatar da cewa gwamnatocin demokradiyya ne kadai za a amince da su tare da tallafawa a yammacin Afirka.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp