A yau ne mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo zai tafi birnin Accra na kasar Ghana domin wakilcin Najeriya a wani babban taron koli na kungiyar ECOWAS kan harkokin siyasa a kasar Mali da sauran sassan yankin.
Wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Laolu Akande ya fitar, ta ce, a wajen taron, Osinbajo zai bi sahun sauran shugabannin kasashen Yammacin Afirka, domin duba irin ci gaban da gwamnatin mulkin sojan Mali ta samu kan komawar kasar bisa tafarkin dimokuradiyya.
Taron zai karba tare da yin la’akari da sabon rahoto daga mai shiga tsakani na ECOWAS a Mali, tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, wanda ya ziyarci Bamako tsakanin 18 zuwa 20 ga watan Maris domin ganawa da shugaban mulkin soja. Shugabannin kasashen za su kuma duba halin da ake ciki a Jamhuriyar Burkina Faso da Guinea.
Bayan da sojoji suka kwace iko da gwamnatoci a Mali, Guinea da Burkina Faso, tare da kakaba takunkumi kan gwamnatin mulkin soja a wadannan kasashe, shugabannin ECOWAS a taron da suka yi na karshe a watan Fabrairu sun tabbatar da cewa gwamnatocin demokradiyya ne kadai za a amince da su tare da tallafawa a yammacin Afirka.