fidelitybank

Taron G20 ya sake fito da haɗin kan duniya wajen kawar da yunwa da talauci – Tinubu

Date:

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce tattaunawar da aka yi a taron G20 a Brazil, ta sake bayyana babbar damar haɗin kai tsakanin ƙasashe don tunkarar ƙalubalen da duniya ke fuskanta gaba ɗaya.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinta na Facebook bayan gabatar da jawabi a taron, Shugaba Tinubu ya ce a taron G20 na bana, Najeriya ta amince da yunƙurin shugaban ƙasar Brazil na neman haɗin kan duniya domin kawar da babbar barazanar da duniya ke fuskanta, wato yunwa da talauci.

”Wannan ƙuduri ya yi daidai da muradin Najeriya na yaƙi da yunwa da talauci, da samar da ci gaba mai ɗorewa ta hanyar samar wa ‘yan Najeriya ayyukan yi”, in ji shi.

Shugaban na Najeriya ya sake jaddada shawarar ƙasashen Afirka na sake fasalin cibiyoyin duniya, ciki har da Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyar G20, don tabbatar da adalci da tafiya da kowa ta yadda Najeriya da ƙasashen Afirka za su shiga a dama da su wajen ɗaukar matakai a waɗanann cibiyoyi.

”A kan sauye-sauyen tattalin arziki, na jaddada ƙudurin Najeriya na tabbatar da adalci a tsarin haraji na duniya da tsarin hada-hadar kuɗi wanda zai cike giɓin da ke tsakanin manyan da ƙananan ƙasashen duniya”.

Shugaba Tinubu ya kuma a yayin da gwamnatinsa ke neman faɗaɗa haraji ta Najeriya ba tare da ƙara wa ‘yan ƙasa wahala ba, gwamnatin ta mayar da hankali kan rage wahalhalu da ɓullo da ƙarin damarmaki da inganta ayyukan more rayuwa, da ƙarfafa ilimi da cibiyoyin tsaro da zamantakewa, waɗanda ya ce suna da mahimmanci don sake farfaɗo da ci gaban ƙasar.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp