Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo na 10 bayan ta doke mai masaukin baƙi Morocco a wasan ƙarshe da aka buga na gasar ta shekara ta 2024, wadda aka jinkirta har ta shigo wannan shekara ta 2025.
Wasan ya tashi ne Najeriya tana da ci uku yayin da Morocco ke da biyu.
Morocco ce ta fara shiga gaba a wasan inda ta zura ƙwallo biyu tun kafin a je hutun rabin lokaci ta ƙafar ƴan wasanta Ghizlane Chebbak da kuma Sanaa Mssoudy.
Sai dai bayan komawa daga hutun rabin lokaci Najeriya ta farke ƙwallon farko ta ƙafar ƴar wasa Esther Okoronkwo kafin daga bisani Folashade Ijamilusi ta zura ƙwallo ta biyu.