fidelitybank

Taribo West ya jagoranci tawagar tsofaffin ƴan wasan Super Eagles zuwa ziyara wajen Bola Tinubu

Date:

Kungiyar tsofaffin ‘yan wasan Super Eagles a karshen mako, sun kai ziyarar ban girma ga dan takarar shugaban kasa, kuma jagoran jam’iyyar (APC) na kasa, Bola Ahmed Tinubu.

A cikin wani faifan bidiyo da aka yada ta yanar gizo, an ga Fasto Taribo West na fadin albarkacin bakinsa a wajen taron neman takarar shugaban kasa na 2023 na Tinubu.

Tsohon dan wasan na Super Eagles ya yi addu’ar Allah ya mayar da Najeriya a matsayin ta ta hannun Tinubu.
Sauran fitattun jiga-jigan ‘yan wasan kwallon kafa na Najeriya da suka halarta akwai Austiin ‘Jay Jay’ Okocha da Kanu Nwankwo, da kuma Victor Ikpeama da Peter Rufai.

Tinubu wanda ke cika shekaru 70 a wannan watan, ya bayyana kudirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa gabanin zaben 2023, kuma akwai shirye-shiryen daukar wani sabon salo na karrama shi.

Haka ma dai wasu daga cikin ‘yan wasan sun kai wa Gwamna Yahaya Bello na Jihar Kogi ziyara a shekarar da ta gabata gabanin wani sabon wasa da aka yi tsakanin ‘yan majalisar zartaswa na jihar da na 1994 da 1996 na tsohon Super Eagles a filin wasa na Confluence dake Lokoja. babban birnin jihar.

A wancan lokacin, an yi ta yada jita-jitar cewa Gwamnan Kogi na shirin tsayawa takarar shugabancin Najeriya a 2023.

Taribo West, wanda ya zakaran UEFA Cup tare da Inter Milan ya zama Fasto bayan kammala kwallon kafa.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp