Jakadun Tarayyar Turai a Najeriya, a jiya sun kai ziyarar ban girma ga mahukuntan kamfanin man fetur na ƙasa (NNPC), inda suka bukaci a inganta hadin gwiwa da Najeriya a fannin makamashi.
Da take jawabi a madadin kungiyar, jakadan EU a Najeriya, Samuela Isopi, ya ce, a sakamakon yanayin siyasar yankin Turai a halin yanzu, nahiyar na sha’awar karfafa hadin gwiwarta da Najeriya musamman a fannin yuwuwar karuwar kayayyakin iskar Gas.
“Najeriya ce kasa ta hudu da ke samar da iskar gas zuwa Turai. Akalla kashi 40 cikin 100 na LNG na Najeriya ana fitar da su zuwa Turai a halin yanzu. Mu ba manyan abokan hulda ne ga Najeriya ba, mu ma manyan abokan hulda ne a bangaren mai da iskar gas, saboda wasu kamfanonin da ke aiki da ku sun fito ne daga Turai.