Tarayyar Turai ta gayyaci shugabannin ƙasasshen nahiyar zuwa birnin Paris a gobe Litinin, domin taron gaggawa kan yaƙin Ukraine.
Hakan tamkar wani martani ne kan yadda Amurka ta ƙi sanya ƙasashen yankin cikin tattaunawar kawo ƙarshen yakin.
Firaministan Birtaniya, Sir Keir Starmer – wanda shi ma zai halarci taron na Faransa – ya kira shi da irin sa na farko cikin shekaru masu yawa.
Mista Starmer na son ganin ya yi amfani da muƙaminsa wajen daidaita Turai da Amurka, domin zama tsintsiya guda kan kawo ƙarshen yaƙin na Ukraine.
A ƙarshen watan nan ne ake sa ran zai kai wa shugaba Trump ziyara a birnin Washington.