Wata tankar mai ta yi sanadiyar mutuwar mutane 17, sakamakon wani mumunan hatsari da ya auku Gun.
Hukumar kula da haddura ta jihar Ogun ta bayyana cewa, ba a iya gane fuskokin wadanda suka mutu. Kawo yanzu, hukumar ta ce, ta na ci gaba da bincike, domin tantance wadanda suka rasa rayukansu.
Jaridar Punch ta rawaito cewa, akalla mutane 17 ne suka kone kurmus a yau Juma’a, yayin da wata tankar mai ta kama wuta a babbar hanyar Legas zuwa Ibadan a jihar Ogun.
Hukumar kiyaye hadurra ta FRSC ta tabbatar da cewa, hatsarin ya afku ne da misalin karfe 5 na safiyar ranar Juma’a kafin isa gadar Isara.