Rundunar ƴan sandan Najeriya reshen jihar Jigawa ta tabbatar da fashewar tankar mai a wani gidan mai da ke Dutse, babban birnin jihar a daren jiya Alhamis.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, kakakin rundunar SP Lawan Shiius Adam ya tabbatar da cewa ba a samu asarar rai ko jikkata ba a haɗarin.
Ya ce tankar ta fashe ne da misalin ƙarfe 7 na dare a gidan man Shakkato da ke kan titin Kiyawa a Dutse a lokacin da tankar ke ƙoƙarin juye man cikin tankin ƙarƙashin ƙasa.
Kakakin rundunar ƴan sandan ya ce bayan samun labarin afkuwar lamarin, tawagar ƴan sandan yankin tare da masu kashe gobara suka yi gaggawar isa wurin inda aka yi nasarar kashe gobarar.
Fashewar tankar mai dai ba sabon abu bane a ƙasar baki ɗaya, inda ko a watan Janairun nan kaɗai an samu fashewar tankar mai aƙalla sau uku, wanda ya janyo asarar rayuka fiye da 80.
Ko a bara ma wata tankar mai ta faɗi a jihar ta Jigawa abin da ya kai ga mutuwar mutane 181.