fidelitybank

Tankar Mai ta kuma yin bindiga a jihar Jigawa

Date:

Rundunar ƴan sandan Najeriya reshen jihar Jigawa ta tabbatar da fashewar tankar mai a wani gidan mai da ke Dutse, babban birnin jihar a daren jiya Alhamis.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, kakakin rundunar SP Lawan Shiius Adam ya tabbatar da cewa ba a samu asarar rai ko jikkata ba a haɗarin.

Ya ce tankar ta fashe ne da misalin ƙarfe 7 na dare a gidan man Shakkato da ke kan titin Kiyawa a Dutse a lokacin da tankar ke ƙoƙarin juye man cikin tankin ƙarƙashin ƙasa.

Kakakin rundunar ƴan sandan ya ce bayan samun labarin afkuwar lamarin, tawagar ƴan sandan yankin tare da masu kashe gobara suka yi gaggawar isa wurin inda aka yi nasarar kashe gobarar.

Fashewar tankar mai dai ba sabon abu bane a ƙasar baki ɗaya, inda ko a watan Janairun nan kaɗai an samu fashewar tankar mai aƙalla sau uku, wanda ya janyo asarar rayuka fiye da 80.

Ko a bara ma wata tankar mai ta faɗi a jihar ta Jigawa abin da ya kai ga mutuwar mutane 181.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp