Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, ya bayar da tallafin Naira miliyan 30 ga iyalan wadanda harin ‘yan bindiga ya rutsa da su a jihar Kebbi.
A ranar Litinin ne ‘yan banga suka yi wa Yan-Sa-Kai kwanton bauna, inda suka kashe 65 daga cikinsu, yayin da a ranar Talata, ‘yan bindigar suka kashe wasu sojoji a jihar.
Tambuwal, ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar jaje ga takwaransa gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu, bisa rasuwar jami’an Yan-Sa-Kai, da kuma jami’an soji da aka kashe a masarautar Zuru.
Gwamnan jihar Sokoto ya bukaci al’ummar jihar da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro hadin kai, domin kara kaimi ga kokarin gwamnatin tarayya da na jihohi wajen yakar wannan barazana.
A nasa martanin Gwamna Abubakar Atiku Bagudu ya ce, jihohin Kebbi da Sokoto, iyali daya ne babba. Ya ce, “Mu iyali daya ne, duk abin da ya shafi daya ya shafi kowa.” a cewar rahoton Daily Trust.