Gwamnatin jihar Sokoto ta ayyana ranar Litinin 1 ga watan Agusta a matsayin ranar da babu aiki domin shiga sabuwar shekarar Musulunci.
Gwamna Aminu Tambuwal ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya sanyawa hannu a ranar Juma’a a Sokoto.
“Bayan tuntubar mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, game da batun jinjirin watan da ke bullar sabuwar watan Musulunci da kuma shekara a yau, na ayyana Litinin 1 ga Agusta, 2022 a matsayin ranar da babu aiki.
“Saboda haka, ina kira ga ’yan’uwanmu da su yi amfani da wannan biki a matsayin wani lokaci na tunane-tunane, bayar da agaji da addu’o’in samun zaman lafiya, wadata da shugabanci na gari.
Ya bukaci mazauna garin da su rika tuna darussan Allah na watan a matsayin daya daga cikin watanni hudu masu alfarma na shekara da aka haramta yaki.