fidelitybank

Tambuwal na alhinin mutuwar Kwamishinansa

Date:

Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal, ya bayyana alhininsa kan rasuwar daya daga cikin kwamishinonin sa, Usman Suleiman.

Jigon jam’iyyar Peoples Democratic Party, wanda ke kula da ma’aikatar harkokin addini, ya rasu ranar Juma’a bayan rashin lafiya.

Tambuwal ya bayyana shi a matsayin musulmi mai kishin addini kuma jajirtaccen jami’i wanda ya yi aiki da kyau a dukkan ma’aikatun da ya jagoranta.

Karanta Wannan: Ina murna da aka kayar da Tambuwal – Fayose

Gwamnan ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar musamman iyalai da makusanta Suleiman.

Tambuwal ya ci gaba da yi masa addu’ar samun lafiya, kuma ya roki Allah Madaukakin Sarki da Ya ba shi Aljannah firdaus ta zama makoma ta karshe.

An yi jana’izar mai rike da sarautar Danmadamin Isa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Wadanda suka halarci jana’izarsa sun hada da Mataimakin Gwamna Mannir Dan’iya da Sakataren Gwamnati Mainasara Ahmad da Shugaban Ma’aikata Abubakar Dan-Shehu da Shugaban Jam’iyyar PDP na Jihar Bello Goronyo da dai sauransu.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp