fidelitybank

Tallafin Mai: Ana biyan sama da biliyan 400 duk wata – NNPCL

Date:

Kamfanin mai na NNPCL na kasa ya ce, adadin kuɗin da ake biya a matsayin tallafin man fetur a kowanne wata ya haura naira biliyan 400.

Kamfanin dillancin labaran NAN ya ruwaito shugaban kamfanin Mele Kyari, na bayyana haka a Abuja babban birnin ƙasar a lokacin kammala sauya wa kamfanin fuska..

Kyari ya ƙara da cewa kamfanin na NNPCL na kashe kusan naira 202 a matsayin tallafi ga kowacce litar mai a faɗin ƙasar

Ya kuma ce a kowacce rana kamfanin na samar da litar mai miliyan 65 domin wadata ƙasar da man fetur.

Shugaban kamfanin ya ce kamfanin zai ci gaba da yin abin da ya wajaba a kansa na samar wa ‘yan ƙasar man da suke buƙata.

Yana mai cewa biyan sama da naira biliyan 400 a kowane wata a matsayin tallafin man na matuƙar yin tarnaƙi ga harkokin kuɗin kamfanin.

Ya ci gaba da cewa, kamfanin na NNPCL shi ne kaɗai kamfanin da ke shigar da mai cikin ƙasar, kuma zai ci gaba da taka rawa cikin shekaru masu zuwa duk da yawan kuɗin tallafin da yake biya.

Mele Kyari ya ce ‘yan kasuwa masu zaman kansu sun daina shigar da mai cikin ƙasar sakamakon wahalar da suke fuskanta wajen samun Dalar Amurka da ake buƙata domin shigar da man zuwa ƙasar.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp