A na sa ran manyan jamiāan kungiyar Taliban za su gana da wakilan Amurka da kasashen Turai a Norway.
Wakilan Taliban mai mutum 15, wanda mukaddashin ministan harkokin ta, Amir Khan Muttaqi ke jagoranta, za su kuma gana da wakilan masu fafutuka na Afghanistan.
Har yanzu babu kasar da ta amince da sabuwar gwamnatin Taliban, to amma wata jamiāar diflomasiyyar Norway, Lisa Golden, ta ce, tattaunawar na da matukar muhimmanci, saboda halin kunci da bukatar taimakon da āyan kasar ke ciki wanda lamarin ke kara muni a kowacce rana.
Majalisar Dinkin Duniya, ta yi gargadin cewa, kasha 95 cikin 100 na āyan Afghanistan ba su da isasshen abinci.