fidelitybank

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Date:

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan’adam da tabbatar da dimokuraɗiyya ta YIAGA Africa ta ce babban zaɓen Najeriya na shekarar 2027 na fuskantar barazana saboda ƙaruwar talauci da rashin tsaro a ƙasar.

YIAGA ta bayyana haka ne a Abuja a lokacin da take gabatar da rahoton bincikenta, inda daraktan ƙungiyar, Samson Itodo ya ce talaucin da ya wa ƴanƙasar katutu zai iya jawo ƙaruwar sayen ƙuri’a a zaɓen, musamman ta hanyar amfani da abinci domin sayen ƙuri’a.

Ya ce, “wannan zaɓen akwai alamar a yi amfani da kuɗi sama da zaɓukan baya. Yanayin talauci da yunwar da ƴanƙasar ke ciki zai sa a samu sauƙin sauya tunanin masu zaɓe,” in ji shi, kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito.

Rahoton ya ƙara da cewa maimakon matsin tattalin arzikin da ƙasar ke ciki ya sa mutane su fusata su fito zaɓe, “akasin hakan za a iya samu, domin ƴansiyasa za su yi amfani da hakan domin sauya musu tunani da kuɗi.”

Rahoton ya kuma bayyana cewa ana samun ƙaruwar ƴanƙasar da suke dawowa rakiyar Hukumar INEC, wanda ƙungiyar ta ce ya ƙaru bayan zaɓukan gwamnonin jihohin Kogi da Edo.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp