Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan’adam da tabbatar da dimokuraɗiyya ta YIAGA Africa ta ce babban zaɓen Najeriya na shekarar 2027 na fuskantar barazana saboda ƙaruwar talauci da rashin tsaro a ƙasar.
YIAGA ta bayyana haka ne a Abuja a lokacin da take gabatar da rahoton bincikenta, inda daraktan ƙungiyar, Samson Itodo ya ce talaucin da ya wa ƴanƙasar katutu zai iya jawo ƙaruwar sayen ƙuri’a a zaɓen, musamman ta hanyar amfani da abinci domin sayen ƙuri’a.
Ya ce, “wannan zaɓen akwai alamar a yi amfani da kuɗi sama da zaɓukan baya. Yanayin talauci da yunwar da ƴanƙasar ke ciki zai sa a samu sauƙin sauya tunanin masu zaɓe,” in ji shi, kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito.
Rahoton ya ƙara da cewa maimakon matsin tattalin arzikin da ƙasar ke ciki ya sa mutane su fusata su fito zaɓe, “akasin hakan za a iya samu, domin ƴansiyasa za su yi amfani da hakan domin sauya musu tunani da kuɗi.”
Rahoton ya kuma bayyana cewa ana samun ƙaruwar ƴanƙasar da suke dawowa rakiyar Hukumar INEC, wanda ƙungiyar ta ce ya ƙaru bayan zaɓukan gwamnonin jihohin Kogi da Edo.