fidelitybank

Talauci da rashin aikin yi ba hujja ba ga ‘Yan damfara – EFCC

Date:

Shugaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC), Abdulrasheed Bawa, ya ce talauci da rashin aikin yi ba hujja ba ce ga shiga cikin damfara da suka shafi kwamfuta.

Kakakin Hukumar, Wilson Uwujaren, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa a Abuja.

Ya ruwaito Bawa yana fadin haka ne a wata lacca mai taken: “Gudunmawar Matasa wajen Yakar Laifukan Tattalin Arziki da Kudade” da aka gabatar a shirin Orientation/Matriculation na sabbin daliban Jami’ar Jihar Legas, Legas.

Bawa ya ce bai kamata talauci ya zama hujjar aikata laifuka ba, kamar yadda rashin aikin yi bai kamata ya zama ginshikin damfarar wasu kudaden shigar da suke samu ba daga matasa masu damfarar yanar gizo.

Shugaban hukumar ta EFCC ya samu wakilcin ACE1 Michael Wetkaz, Kwamandan shiyyar Legas na EFCC.

Ya kuma bayyana matasa a matsayin daya daga cikin masu ruwa da tsaki a harkar gina kasa, inda ya kara da cewa za su iya tinkarar matsalar cin hanci da rashawa idan suka nuna aniyarsu ta zama ’yan canji a harkokinsu daban-daban.

“Ba za ku iya magance duk wani laifi da kuke aikatawa ba. Zama wakilan canji ta ƙin shiga, sauƙaƙe ko aiwatar da kowane nau’i na laifukan tattalin arziki.

“A cikin mu’amalarku a ciki da wajen makarantar, ku nisanta daga aikata laifuka. Ta wannan hanyar, zaku iya yin tasiri ga duk wanda ke kusa da ku, “in ji shi.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp