Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana a jiya cewa, talakawan Najeriya miliyan 83 ne za su ci gajiyar dokar hukumar inshorar lafiya ta kasa ta 2022 da ya sanya wa hannu.
Dokar Hukumar Inshorar Lafiya ta Kasa ta 2022 ta maye gurbin da aka soke dokar tsarin inshorar lafiya ta kasa Cap N42, Dokokin Tarayyar Najeriya 2004.
Yayin da yake rattaba hannu a kan dokar ta zama doka, shugaban ya ce, da sabuwar dokar, za a kafa wani asusu “domin tabbatar da daukar nauyin talakawan Najeriya miliyan 83, wadanda ba za su iya biyan kudaden alawus-alawus kamar yadda Hukumar Lancet Nigeria ta ba da shawarar ba.”
Wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Mallam Garba Shehu, ya fitar, ta ruwaito Buhari na cewa: “Ga dimbin marasa galihu da ba za su iya biyan kudaden inshorar lafiya ba, za a samar da wani asusun kungiyar masu rauni. har ya hada da wani bangare na Asusun Bayar da Kiwon Lafiya na asali na Hukumar, Levy na Inshorar Lafiya, Asusun Tallafawa na Musamman, da duk wani abin hannun jari, gudummawa da kyaututtuka ga Hukuma.”