fidelitybank

Takarar shugabancin APC: Kawunan ƴan majalisar dokoki ya rabu gida 3

Date:

Mambobin majalisar dokokin kasar nan sun samu rarrabuwar kawuna, dangane da fitowar ‘yan takarar shugabancin jam’iyyar APC na kasa har su uku daga majalisar tarayya.

Jam’iyyar APC ta ce, za ta zabi sabon kwamitin ayyuka na kasa karkashin jagorancin shugaban a babban taronta na kasa da aka shirya yi a ranar Asabar.

‘Yan takarar uku wadanda dukkansu ‘yan majalisar dattawa ne, Abdullahi Adamu, Sani Musa da Tanko Al-Makura.

Sanatocin dai wadanda dukkaninsu sun fito ne daga shiyyar Arewa ta tsakiya, sun fafata ne da wasu masu neman tsayawa jam’iyya mai mulki, wadanda ba ‘yan majalisar tarayya ba.

A makon da ya gabata ne Adamu da Al-Makura suka gana da jiga-jigan jam’iyyar APC a majalisar wakilai, inda daga bisani suka ba wa ‘yan majalisar tikitin tsayawa takara, idan ya zama shugaban jam’iyyar. Har yanzu Musa bai gana da kwamitin ba.

Al-Makura da Adamu tsoffin gwamnonin jihar Nasarawa ne.bYayin da Al-Makura ke wakiltar mazabar Nasarawa ta tsakiya, Adamu yana wakiltar mazabar Nasarawa ta Yamma a majalisar dattawa.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp