Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Mista Ayo Fayose, da Sanata Dino Melaye sun shiga carcar baka, kan kalaman batanci ga Alhaji Atiku Abubakar da Bukola Saraki.
Ana zargin Fayose da nuna sha’awar sa na daga tutar jam’iyyar PDP a zaben 2023, ya yi kalamai marasa dadi ga Atiku Abubakar da Bukola Saraki.
Amma Sanata Melaye a martanin da ya yi wa Fayose, ya fitar da sanarwar manema labarai ranar Juma’a, yana mai cewa, “Shugabancin kasa ba Ponmo da Amala bane.”
Dino a cikin sanarwar ya caccaki Fayose bisa zargin bata sunan, Alhaji Atiku Abubakar da Sanata Bukola Saraki a kalaman sa na baya-bayan nan.
Ya ce, su biyun sun zarce matakin siyasar Fayose, kuma shugabancin Najeriya ba na masu kishin mutane irin su Fayose bane.
Ya ce, “Batun da ke gaban ‘yan Najeriya a yanzu ba wai wanda zai iya cin abinci ba, sai wanda zai iya samar da abinci. Don haka ne ma, Atiku Abubakar ya samu a matsayin tsohon mataimakin shugaban kasa da kuma Bukola Saraki a matsayin tsohon shugaban majalisar dattawa da Fayose ya yi a matsayin zagon kasa a matsayin dan wasan cacar shugaban kasa.
“A bayyane yake daga makami mai linzami da Fayose ya tura cewa, kawai ya kawar da ‘yan takarar sa na gaba a PDP ne a matsayin wata dabbar da za ta iya kawo wa ubangidansa na siyasa dama a APC.