fidelitybank

Takarar Al-Mustapha da ƴan jam’iyyar AA ta shiga tsilla-tsilla

Date:

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ta yi watsi da sunayen ‘yan takarar jam’iyyar Action Alliance (AA), ciki har da sunan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Manjo Hamza Al-Mustapha mai ritaya.

Sai dai wannan umarni da aka bai wa ‘yan jarida a Kaduna a ranar Asabar din da ta gabata, ya umurci hukumar zaben ta nuna jerin sunayen ‘yan takarar da shugabancin jam’iyyar a karkashin Adekunle Rufai Omoaje ya mika mata.

Hukumar zaben ta hanyar kin amincewa da jerin sunayen ‘yan takarar da bangaren Omoaje ya gabatar mata, a cewar kotun da ke karkashin Mai shari’a Z.B. Abubakar.

Mai shari’a Abubakar wanda ya bayar da misali da sashe na 29 (1) na dokar zabe, 2022, ya umurci INEC da ta gaggauta buga sunaye da adireshi na dukkan ‘yan takarar da Omoaje ya mika a madadin kungiyar Action Alliance.

“Ta hanyar tanadin sashe na 29 (1) na dokar zabe, 2022, ya kamata INEC ta buga ta hanyar nunawa a ofishin da ya dace na INEC da kuma a shafinta na intanet.”

A cewar hukuncin kotun, akwai yiwuwar jerin sunayen ‘yan takarar da Omoaje ya bayar zai maye gurbin ‘yan takarar INEC da aka riga aka bayyana, ciki har da dan takarar shugaban kasa, Manjo Hamza Al-Mustapha mai ritaya.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...

Duk wahala sai dai mu mutu a Gaza – Fatma

Wata mai mai ƴaƴa tara ta ce, duk runtsi...

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...
X whatsapp