Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ta yi watsi da sunayen ‘yan takarar jam’iyyar Action Alliance (AA), ciki har da sunan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Manjo Hamza Al-Mustapha mai ritaya.
Sai dai wannan umarni da aka bai wa ‘yan jarida a Kaduna a ranar Asabar din da ta gabata, ya umurci hukumar zaben ta nuna jerin sunayen ‘yan takarar da shugabancin jam’iyyar a karkashin Adekunle Rufai Omoaje ya mika mata.
Hukumar zaben ta hanyar kin amincewa da jerin sunayen ‘yan takarar da bangaren Omoaje ya gabatar mata, a cewar kotun da ke karkashin Mai shari’a Z.B. Abubakar.
Mai shari’a Abubakar wanda ya bayar da misali da sashe na 29 (1) na dokar zabe, 2022, ya umurci INEC da ta gaggauta buga sunaye da adireshi na dukkan ‘yan takarar da Omoaje ya mika a madadin kungiyar Action Alliance.
“Ta hanyar tanadin sashe na 29 (1) na dokar zabe, 2022, ya kamata INEC ta buga ta hanyar nunawa a ofishin da ya dace na INEC da kuma a shafinta na intanet.”
A cewar hukuncin kotun, akwai yiwuwar jerin sunayen ‘yan takarar da Omoaje ya bayar zai maye gurbin ‘yan takarar INEC da aka riga aka bayyana, ciki har da dan takarar shugaban kasa, Manjo Hamza Al-Mustapha mai ritaya.