Rahotanni daga jihohi da dama a fadin tarayyar kasar nan sun nuna cewa, akalla Kwamishinoni 53, da ma’aikatan gwamnoni da dama ne suka ajiye aikinsu domin tsayawa takara a zaben 2023.
Hakan ya faru ne bayan wasu gwamnoni sun bukac e su sauka daga mukamansu domin yin biyayya da sashe na 84(12) na dokokin zabe da ya umarci masu sha’awar su yi murabus.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ministocin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari da ake ganin suna son tsayawa takara, suke ci gaba da zama a kan mukamansu.
Cikinsu akwai Ministan Sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi, Ministan Kwadago, Sanata Chris Ngige; da Ministan Shari’a Abubakar Malami, da sauran masu rike da manyan mukamai a hukumomin gwamnati da suka fara hararo wasu daga cikin kujerun siyasa da suka hada da ta shugaban kasa, da gwamnoni da ‘yan majalisu da sauran.
Rahotanni sun nuna cewa Kwamishinoni da masu ba da shawara akalla 12 ne suka mika wa Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq na Jihar Kwara takardun murabus.
A jihar Kano, bayanai sun nuna cewa akalla Kwamishinoni 10 ne suka ajiye aiki cikinsu har da Mataimakin Gwamna Nasir Gawuna, wanda shi ne Kwamishinan Noma.
A Delta, rahotanni sun ce shugaban ma’aikatan gwamnan jihar Ovie Agas,da Kwamishinoni tara sun sauka daga kujerunsu domin tsayawa takarar a zaben 2023.