fidelitybank

Takarar 2023: Kwamishinoni 53 da hadiman gwamnoni sun ajiye aikin su

Date:

Rahotanni daga jihohi da dama a fadin tarayyar kasar nan sun nuna cewa, akalla Kwamishinoni 53, da ma’aikatan gwamnoni da dama ne suka ajiye aikinsu domin tsayawa takara a zaben 2023.

Hakan ya faru ne bayan wasu gwamnoni sun bukac e su sauka daga mukamansu domin yin biyayya da sashe na 84(12) na dokokin zabe da ya umarci masu sha’awar su yi murabus.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ministocin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari da ake ganin suna son tsayawa takara, suke ci gaba da zama a kan mukamansu.

Cikinsu akwai Ministan Sufurin Najeriya, Rotimi Amaechi, Ministan Kwadago, Sanata Chris Ngige; da Ministan Shari’a Abubakar Malami, da sauran masu rike da manyan mukamai a hukumomin gwamnati da suka fara hararo wasu daga cikin kujerun siyasa da suka hada da ta shugaban kasa, da gwamnoni da ‘yan majalisu da sauran.

Rahotanni sun nuna cewa Kwamishinoni da masu ba da shawara akalla 12 ne suka mika wa Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq na Jihar Kwara takardun murabus.

A jihar Kano, bayanai sun nuna cewa akalla Kwamishinoni 10 ne suka ajiye aiki cikinsu har da Mataimakin Gwamna Nasir Gawuna, wanda shi ne Kwamishinan Noma.

A Delta, rahotanni sun ce shugaban ma’aikatan gwamnan jihar Ovie Agas,da Kwamishinoni tara sun sauka daga kujerunsu domin tsayawa takarar a zaben 2023.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp