Da yammacin ranar Talata wasu gine-gine guda biyu a unguwar Badalar ‘Dan Agundi da ke Kano sun ruguje bisa ga wani lamari da ba a sani ba.
Shedun gani da ido sun bayyana cewa jami’an tsaro dauke da muggan makamai, sun kama jami’in tsaron wurin, inda suka tsare shi kafin fara aikin rusa ginin.
A cewar gidan rediyon Arewa, a halin yanzu filayen da abin ya shafa na fuskantar takaddamar shari’a tsakanin masu kadarorin da Hukumar Tsare-tsare da Raya Birane ta Jihar Kano (KNUPDA).
Tun hawansa mulki, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna aniyar rusa gine-gine a yankin Badalar ‘Dan Agundi zuwa Kofar Fanfo, inda ya bayyana cewa gwamnatin da ta gabata ce ta ware filayen da ake magana a kai.
Ya zuwa yanzu dai babu wata hukuma da ta dauki alhakin rusa ginin.
Sai dai ana ci gaba da nuna damuwa a tsakanin al’ummar yankin dangane da yadda ake aiwatar da rusasshiyar da daddare, lamarin da ya kara dagula rigingimun mallakar filaye. A cewar Daily Post.