fidelitybank

Tabbas ta fara biyan kudin sabulu a wajen al’umma – Tinubu

Date:

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya taya al’umma musulmi murnar fara azumin watan Ramadan na shekarar 2025, inda ya yi addu’ar Allah ya sa azumin ya zo da albarka.

Shugaban ya bayyana haka ne a wani saƙo ya fitar, inda a ciki ya ce kwalliya ta fara biyan kuɗin sabulu game da manufufin gwamnatinsa.

Ya ce, “muna godiya ga Allah da ya nuna mana farkon wannan azumin lafiya, wanda ya zo a daidai lokacin da muke ƙokarin inganta ƙasarmu. A game da manufofin da muka ɗauka masu tsauri, kwalliya ta fara biyan kuɗin sabulu domin tattalin arzikin ƙasarmu ya fara inganta.

“Haka kuma farashin abinci, wanda a baya ya yi tashin gwauron zabi, yanzu ya fara sauka, wanda hakan sauƙi ne ga masu azumi da ma sauran ƴan Najeriya baki ɗaya. Naira na ƙara samun daraja, sannan farashin man fetur na raguwa. Duk waɗannan abubuwan suna nuna cewa akwai haske ne a gaba,” in ji shi.

Shugaban ya kuma yi kira ga musulmi da su yi amfani da watan wajen ƙara imani da tausayin juna da kuma yin addu’a domin ci gaban ƙasa.

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp