fidelitybank

Tabbas na hakkewa Karnuka – Ɗan Birtaniya

Date:

Wani sanannen mai nazari kan rayuwar kadoji ɗan asalin Birtaniya, ya amsa tuhumar da ake yi masa ta yin lalata da dabbobi da kuma mallakar abubuwan da suka jiɓanci cin zarafin yara.

Wata kotu a ƙasar Australiya ce ta saurari ƙarar, kan cewa Adam Britton ya ɗauki bidiyon kansa yana azabtar da gwamman karnuka har kusan dukkanin su suka mutu.

Haka nan mutumin ya riƙa wallafa irin waɗannan bidiyoyi a shafukan intanet.

Yanzu haka dai ana jiran kotu ta ajiye ranar da za ta yanke hukunci a kan mutumin, wanda ya taɓa yin aiki da BBC da kuma tashar talabijin mai shirye-shirye kan rayuwar dabbobi ta National Geographic.

A lokacin sauraron ƙarar a ranar Litinin, alƙalin kotun ya ce yawancin bidiyon da aka kawo a matsayin shaida sun yi muni da yawa, inda aka gargaɗi mahalarta kotun kan cewa za su iya fita domin gudun kada hankulansu su tashi.

Alƙalin kotun, mai shari’a Michael Grant ya ce ya damu kan cewa bayanan abubuwan da Britton ya aikata za su iya haifar da mummunar damuwa ga mahalarta kotun, inda ya buƙaci jami’an tsaro da ƙananan ma’aikatan kotun da su fita daga zauren.

Masu gabatar da ƙara sun ce Britton ya kasance mai ‘matsananciyar muguwar aniya da son yin lalata da dabbobi’ tun aƙalla shekarar 2014.

Sun ce baya ga cin zarafin nasa dabbobin, ya kuma shawo kan wasu mutane daban domin su ba shi ajiyar dabbobinsu, waɗanda su ma ya ci zarafin su.

An tabbatar da cewa ya riƙa cin zarafin dabbobin ne a wani ɗakin kwantena da ya mallaka, wanda ya maƙala wa kyamarori, kuma ya laƙaba wa wurin sunan “ɗakin azabtarwa.”

An bayyana cewa daga cikin karnuka 42 da ya ci zarafi a tsawon wata 18, guda 39 sun mutu.

Yanzu haka dai ana tsare da Briiton tun bayan da aka kama shi, inda ake sa ran yanke masa hukunci a watan Disamba.

An haife shi ne a yankin West Yorkshire na Birtaniya, inda ya koma Australia shekaru 20 da suka gabata domin yin aikin da ya shafi kadoji.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...
X whatsapp