fidelitybank

Tabbas na hakkewa Karnuka – Ɗan Birtaniya

Date:

Wani sanannen mai nazari kan rayuwar kadoji ɗan asalin Birtaniya, ya amsa tuhumar da ake yi masa ta yin lalata da dabbobi da kuma mallakar abubuwan da suka jiɓanci cin zarafin yara.

Wata kotu a ƙasar Australiya ce ta saurari ƙarar, kan cewa Adam Britton ya ɗauki bidiyon kansa yana azabtar da gwamman karnuka har kusan dukkanin su suka mutu.

Haka nan mutumin ya riƙa wallafa irin waɗannan bidiyoyi a shafukan intanet.

Yanzu haka dai ana jiran kotu ta ajiye ranar da za ta yanke hukunci a kan mutumin, wanda ya taɓa yin aiki da BBC da kuma tashar talabijin mai shirye-shirye kan rayuwar dabbobi ta National Geographic.

A lokacin sauraron ƙarar a ranar Litinin, alƙalin kotun ya ce yawancin bidiyon da aka kawo a matsayin shaida sun yi muni da yawa, inda aka gargaɗi mahalarta kotun kan cewa za su iya fita domin gudun kada hankulansu su tashi.

Alƙalin kotun, mai shari’a Michael Grant ya ce ya damu kan cewa bayanan abubuwan da Britton ya aikata za su iya haifar da mummunar damuwa ga mahalarta kotun, inda ya buƙaci jami’an tsaro da ƙananan ma’aikatan kotun da su fita daga zauren.

Masu gabatar da ƙara sun ce Britton ya kasance mai ‘matsananciyar muguwar aniya da son yin lalata da dabbobi’ tun aƙalla shekarar 2014.

Sun ce baya ga cin zarafin nasa dabbobin, ya kuma shawo kan wasu mutane daban domin su ba shi ajiyar dabbobinsu, waɗanda su ma ya ci zarafin su.

An tabbatar da cewa ya riƙa cin zarafin dabbobin ne a wani ɗakin kwantena da ya mallaka, wanda ya maƙala wa kyamarori, kuma ya laƙaba wa wurin sunan “ɗakin azabtarwa.”

An bayyana cewa daga cikin karnuka 42 da ya ci zarafi a tsawon wata 18, guda 39 sun mutu.

Yanzu haka dai ana tsare da Briiton tun bayan da aka kama shi, inda ake sa ran yanke masa hukunci a watan Disamba.

An haife shi ne a yankin West Yorkshire na Birtaniya, inda ya koma Australia shekaru 20 da suka gabata domin yin aikin da ya shafi kadoji.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp