fidelitybank

Tabbas Dangote ya samar da sauki ga ‘yan kasa na rage farashin man fetur – NLC

Date:

Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), reshen Lagos, ta yabawa Matatar Dangote bisa saukar farashin mai da aka yi kwanan nan, tana mai bayyana wannan a matsayin taimako ga tattalin arzikin ’yan Najeriya a wannan lokaci na kunci.

Shugabar NLC ta jihar Lagos, Funmi Sessi, wacce ta yi wannan yabon cikin wata sanarwa a ranar Laraba, ta ce zuwan Matatar Dangote a wannan lokaci ya na muhimmanci kwarai da gaske.

Sessi ta bayyana fatan cewa saukar farashin zai rage kudin sufuri, farashin kaya tare da bayar da rangwame ga ’yan Najeriya da ke fama da tsadar rayuwa.

“Wannan sauyin farashin ya kasance wani muhimmin taimako ga miliyoyin ’yan Najeriya da suka dade suna fama da tsadar mai da kuma tsadar rayuwa.

“Idan ba don matatar Dangote ba, muna ganin gwamnati na iya ci gaba da shigo da mai daga ƙasashen waje.

“Amma yanzu, Dangote na samar da kimanin ganguna 650,000 na mai a kowace rana, yayin da matatun mai na Fatakwal da wasu da aka gyara ke samar da kusan ganguna 210,000 a rana, wanda ba ya kai rabin abin da Dangote ke samarwa.

“Da wannan, Dangote ya kawo gasa mai kyau a cikin bangaren, kuma mun fara ganin raguwar farashin mai,” in ji ta.

Shugabar ta kuma lura cewa matatar Dangote ta fara fitar da mai zuwa kasashe kamar Ghana, Togo, da sauran su.

A cewarta, wannan yana nufin cewa za a samu dagawar darajar kudin kasar.

“A wannan lokaci, muna yaba wa Dangote. Muna kuma godiya bisa wannan matakin da ya dauka cikin lokaci.

“Kada kuma mu manta cewa Majalisar Dokoki ta Kasa tana kokarin fitar da kudiri da zai tilasta amfani da kudin Najeriya a cikin gida.

“Abin takaici ne cewa kudinmu ya rasa ƙarfinsa, har a yankin Yammacin Afirka.

“Don haka, ya kamata gwamnati ta karfafa wa Dangote da sauran masu zuba jari da ke shigowa don tabbatar da gasa mai kyau.

“Muna maraba da wannan rangwamen, wanda zai taimaka wa ’yan Najeriya da ke fama da tsadar rayuwa, kuma muna kira ga sauran masu ruwa da tsaki su kwaikwayi abin da Dangote ke yi don amfanin kowa,” in ji Sessi.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp