fidelitybank

Tabbas an samu bullar cutar Anthrax a Najeriya – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da ɓullar cutar anthrax a hukumance.

Wata sanarwa da ma’aikatar noma da raya karkara ta ce an kai rahoton dabbobin da ke nuna alamun yiwuwar kamuwa da cutar anthrax a wata gona da ke Suleja a Jihar Neja zuwa ofishin babban jami’in kula da dabbobi na Najeriya a ranar 14 ga watan Yuli.

Jaridar daily trust ta ruwaito cewa ma’aikatar ta ce lamarin ya faru ne a wata gonar dabbobi da ta ƙunshi shanu da tumaki da awaki da ke Gajiri a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna a ƙaramar hukumar Suleja a jihar Neja, inda wasu daga cikin dabbobin ke da alamomi da suka haɗa da zubar jini daga sassan jikinsu, hanci, idanu da kunnuwa.

Ta ce tawagar masu bayar da agajin gaggawa da ta haɗa da ƙwararrun ma’aikatan lafiya na tarayya da na jihar sun ziyarci gonar don gudanar da bincike na farko tare da tattara samfurori daga dabbobin da suka kamu da cutar.

Ma’aikatar ta ce gwaje-gwaje na Cibiyar Nazarin Dabbobi ta ƙasa ta tabbatar da kamuwa da cutar, “wanda ke nuna alamar cutar anthrax ta farko a Najeriya a cikin ‘yan shekarun nan”.

Ta yi nuni da cewa, gwamnatin tarayya ta yi gargaɗi ga ‘yan Najeriya makonnin da suka gabata bayan samun labarin ɓarkewar cutar anthrax a Arewacin Ghana inda duk dabbobin da suka kamu da cutar suka mutu.

Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnati ta yi kira ga ƴan Najeriya da su gaggauta kai rahoton bullar dabbobin da ke zubar da jini a jikinsu ga hukumomin kiwon lafiyar dabbobi ko kuma ma’aikatan aikin gona.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp