Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya kai ziyara Kwankaso a karamar hukumar Madobi, domin yi wa iyalan marigayi Inuwa Musa Kwankaso wanda kani ne ga tsohon gwamna jihar.
Yayin ganawa da manema labarai ya ce, rashin marigayin a matsayin babban rashi ba ga iyalan mamacin kadai ba har ma da al’ummar Kano baki daya
Abdullahi Umar Ganduje ya kuma bukaci iyalan marigayin da su jurewa rashin marigayin tare da cigaba da yi masa addu’a.
Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ziyarci wurin ta’aziyar tare da tawagar jami’an gwamnatin Kano.