Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gayyaci gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma kan barnata dukiya da rayuka da ‘yan bindiga suka yi a Imo.
Shugaban ya bayyana damuwarsa kan tashe-tashen hankula da ke kunno kai a yankin Gabashin Najeriya.
Buhari ya kuma gayyaci Ministan Wutar Lantarki, Abubakar Aliyu, da babban mai ba da shawara kan tattalin arziki, Farfesa Doyin Salami, zuwa wani taro a fadar shugaban kasa.
Za a yi taron na daban ne a Villa nan gaba a ranar Litinin.
Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Garba Shehu ya fitar, ta ce, shugaban kasar a lokacin da yake yin Allah wadai da yawaitar tashe-tashen hankula a jihar Imo, sakamakon lalata gine-gine da kaddarorin ‘yan sanda da gidan Farfesa George Obiozor, shugaban kungiyar Ohaneze Ndigbo. , yayi alkawarin duba yanayin tsaro a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya.
Buhari ya kuma bayyana damuwarsa kan matsalar wutar lantarki da ake yawan samu, inda ya nemi gafarar ‘yan Najeriya tare da bada tabbacin samun sauki cikin gaggawa.