Rahotanni daga jihar Filato na nuni da cewa ƴan bindiga sun sace tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Filato a zaɓen 2019, Nkemi Nicholas Nashe.
Jaridar Punch ta rawaito cewa, wani makusancin Mista Nshe na cewa, jama’ na zaman fargaba tun bayan faruwar wannan lamari a Shendam.
Mista Nashe wanda jigo ne a Jam’iyyar PDP, ya taɓa riƙe muƙamin Shugaban Ƙaramar Hukumar Shendam a baya.
Shi kansa gwamnan jihar mai ci a yanzu Simon Lalong ya fito ne daga Ƙaramar Hukumar Shendam.
Sace Mista Nshe na zuwa ne ƙwanaki kaɗan, tun bayan sakin wani basarake a jihar ta Filato da a ka sace, Charles Mato Dakat.
Sai dai sojoji da ke jihar sun bayyana cewa sun kama mutum takwas da su ke zargi da hannu a sace basaraken. Kamar yadda BBC ta rawaito.